Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Kor 4:17-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Saboda haka, na aika muku da Timoti, wanda yake shi ne ɗana ƙaunatacce, amintacce kuma a cikin Ubangiji, zai kuwa tuna muku da ka'idodina na bin Almasihu, kamar yadda nake koyarwa a ko'ina, a kowace ikkilisiya.

18. Waɗansu har suna ɗaga kai, kamar ba zan zo wurinku ba.

19. Amma kuwa zan zo gare ku ba da daɗewa ba, in Ubangiji ya yarda, zan kuma bincika, in ga ƙarfin mutane masu ɗaga kan nan, ba maganganunsu ba.

20. Domin Mulkin Allah ba ga maganar baka yake ba, sai dai ga ƙarfi.

21. To, me kuka zaɓa, in zo muku da sanda, ko kuwa da fuskar ƙauna da lumana?

Karanta cikakken babi 1 Kor 4