Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Kor 15:8-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Daga ƙarshen duka ya bayyana a gare ni, ni ma da nake kasasshe, marar cancanta.

9. Don ni ne mafi ƙanƙanta a cikin manzanni, ban ma isa a ce da ni manzo ba, saboda na tsananta wa Ikkilisiyar Allah.

10. Amma saboda alherin Allah na zama yadda nake, alherin da ya yi mini kuwa ba a banza yake ba. Har ma na fi kowannensu aiki, ba kuwa ni ba, alherin Allah ne da yake zuciyata.

Karanta cikakken babi 1 Kor 15