Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Kor 15:4-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. cewa an binne shi, an ta da shi a rana ta uku, kamar yadda Littattafai suka faɗa,

5. ya kuma bayyana ga Kefas, sa'an nan ga sha biyun.

6. Sa'an nan ya bayyana ga 'yan'uwa fiye da ɗari biyar a lokaci guda, yawancinsu kuwa suna nan har zuwa yanzu, amma waɗansu sun yi barci.

7. Sa'an nan ya bayyana ga Yakubu, sa'an nan ga dukan manzanni.

8. Daga ƙarshen duka ya bayyana a gare ni, ni ma da nake kasasshe, marar cancanta.

9. Don ni ne mafi ƙanƙanta a cikin manzanni, ban ma isa a ce da ni manzo ba, saboda na tsananta wa Ikkilisiyar Allah.

Karanta cikakken babi 1 Kor 15