Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Kor 15:35-38 Littafi Mai Tsarki (HAU)

35. Watakila wani zai yi tambaya, “Ta yaya ake ta da matattu? Da wace irin kama kuma suke fitowa?”

36. Kai, marar azanci! Abin da ka shuka, ai, ba zai tsiro ba sai ya mutu.

37. Abin da ka shuka kuma, ba shi ne ainihin abin da zai kasance ba, ƙwaya ce ƙawai, ko ta alkama ce, ko kuma, wata iri dabam.

38. Amma Allah yakan ba ta kama, yadda ya nufa, kowace ƙwaya da irin tata kama.

Karanta cikakken babi 1 Kor 15