Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 14:7-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. “Akwai sa zuciya ga itacen da aka sare,Yana iya sāke rayuwa ya yi toho.

8. Ko da yake saiwoyinsa sun tsufa,Kututturensa kuma ya ruɓe a ƙasa,

9. In aka zuba ruwa, sai ya toho kamar sabon tsiro.

10. Amma ɗan mutum ya mutu, ƙarshensa ke nan,Ya mutu, a ina yake a lokacin nan?

11. “Mai yiwuwa ne koguna za su daina gudu,Har tekuna kuma su ƙafe.

12. Amma matattu ba za su tashi ba daɗai,Ba za su ƙara tashi ba sam, muddin sararin sama na nan.Sam, ba za a dame su cikin barcinsu ba.

13. “Ya Allah, da ma a ce ka ɓoye ni a lahira,Ka bar ni a ɓoye, har fushinka ya huce,Sa'an nan ka sa lokacin da za ka tuna da ni!

14. Idan mutum ya mutu, zai sāke rayuwa kuma?Amma zan jira lokaci mafi kyau,In jira sai lokacin wahala ya wuce.

15. Sa'an nan za ka yi kira, ni kuwa zan amsa,Za ka yi murna da ni, ni talikinka.

16. Sa'an nan za ka lura da kowace takawataAmma ba za ka bi diddigin zunubaina ba.

17. Za ka soke zunubaina ka kawar da su,Za ka shafe dukan kurakuran da na taɓa yi.

18. “Lokaci na zuwa sa'ad da duwatsu za su fāɗi,Har ma za a kawar da duwatsun bakin teku.

19. Ruwa zai zozaye duwatsu, su ragu,Ruwan sama mai ƙarfi zai kwashe jigawa,Kai ma ka bar mutane, ba su da sauran sa zuciya ko kaɗan.

Karanta cikakken babi Ayu 14