5. Amma zai ce, ‘Ni ba annabi ba ne, ni manomi ne, gama ƙasa abar mallakata ce tun ina yaro.’
6. Idan wani ya tambaye shi cewa, ‘Waɗannan raunukan da suke a hannuwanka fa?’ Zai ce, ‘Ai, raunuka ne da aka yi mini a gidan abokaina.’ ”
7. “Ka farka, ya kai takobi, ka fāɗa wa makiyayina,Ka fāɗa wa mutumin da yake kusa da ni,Ka sari makiyayin domin tumakin su watse.Zan bugi ƙanana da hannuna,Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.