Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 94:3-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Har yaushe mugaye za su yi ta murna?Har yaushe ne, ya Ubangiji?

4. Har yaushe za su yi shakiyanci,Su yi ta ɗaga kai?Har yaushe, ya Ubangiji?

5. Suna ragargaza jama'arka, ya Ubangiji,Suna zaluntar waɗanda suke naka.

6. Suna karkashe gwauraye, wato matan da mazansu suka mutu, da marayu,Da kuma baƙin da suke zaune a ƙasarmu.

7. Suna cewa, “Ai, Ubangiji ba ya ganinmu,Allah na Isra'ila ba ya lura da abin da yake faruwa!”

8. Ya jama'ata, ƙaƙa kuka zama dakikai, wawaye haka?Sai yaushe za ku koya?

9. Allah ya yi mana kunnuwa, shi ba zai ji ba?Allah ya yi mana idanu, shi ba zai gani ba?

10. Shi ne yake shugabancin sauran al'umma, ba zai hukunta su ba?Shi ne yake koya wa dukan mutane, shi ba shi da sani ne?

11. Ubangiji ya san tunaninsu,Ya san kuma hujjojinsu na rashin hankali.

12. Ya Ubangiji, mai farin ciki ne mutumin da kake koya wa,Mutumin da kake koya masa shari'arka.

Karanta cikakken babi Zab 94