Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 92:9-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

9. Mun sani maƙiyanka za su mutu,Dukan mugaye kuwa za a yi nasara da su.

10. Ka sa ni na yi ƙarfi kamar bijimi mai faɗa,Ka sa mini albarka da farin ciki.

11. Na ga fāɗuwar maƙiyana,Na ji kukan mugaye.

12. Adalai za su yi yabanyaKamar itatuwan giginya,Za su yi girma kamar itatuwan al'ul na Lebanon.

13. Za su zama kamar itatuwan da aka daddasa a Haikalin Ubangiji,Suna ta yabanya a Haikalin Allahnmu.

14. Waɗanda suke yin 'ya'ya da tsufansu,A kullum kuwa kore shar suke,Suna da ƙarfinsu kuma.

15. Wannan ya nuna Ubangiji adali ne,Shi wanda yake kāre ni,Ba kuskure a gare shi.

Karanta cikakken babi Zab 92