Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 89:25-41 Littafi Mai Tsarki (HAU)

25. Zan faɗaɗa mulkinsa tun daga Bahar Rum,Har zuwa Kogin Yufiretis.

26. Zai ce mini, ‘Kai ubana ne da Allahna,Kai ne kake kiyaye ni, kai ne Mai Cetona.’

27. Zan maishe shi ɗan farina,Mafi girma daga cikin dukan sarakuna.

28. Zan riƙa ƙaunarsa har abada,Alkawarin da na yi da shi kuma zai tabbata har abada.

29. A kullayaumin daga cikin zuriyarsa ne za a naɗa sarki,Mulkinsa zai dawwama kamar sararin sama.

30. “Amma idan zuriyarsa sun ƙi yin biyayya da shari'ata,Ba su kuwa zauna cikin ka'idodina ba,

31. In sun ƙyale koyarwata,Ba su kiyaye umarnaina ba,

32. To, sai in hukunta su saboda zunubansu,Zan bulale su saboda laifofinsu.

33. Amma fa, ba zan daina ƙaunar Dawuda ba,Ba kuwa zan rasa cika alkawarin da na yi masa ba.

34. Ba zan keta alkawarin da na yi masa ba,Ba zan soke ko ɗaya daga cikin alkawaran da na yi masa ba.

35. “Da sunana mai tsarki na yi alkawari sau ɗaya tak,Ba zan yi wa Dawuda ƙarya ba!

36. Zuriyarsa za ta kasance kullum,Zan lura da mulkinsa muddin rana tana haskakawa.

37. Zai dawwama kamar wata,Kamar amintaccen mashaidin nan da yake a sararin sama.”

38. Amma kana fushi da zaɓaɓɓen sarkinka,Ka rabu da shi, ka yashe shi.

39. Ka soke alkawarinka wanda ka yi wa bawanka,Ka jefar da kambinsa a cikin ƙazanta.

40. Ka rurrushe garun birninsa,Ka mai da sansaninsa mai kagara kufai.

41. Dukan waɗanda suke wucewa za su sace masa kayansa,Maƙwabtansa duka suna yi masa ba'a.

Karanta cikakken babi Zab 89