Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 89:23-32 Littafi Mai Tsarki (HAU)

23. Zan ragargaza magabtansa,In karkashe duk waɗanda suke ƙinsa.

24. Zan ƙaunace shi kullum, in amince da shi,Zan sa ya yi nasara kullayaumin.

25. Zan faɗaɗa mulkinsa tun daga Bahar Rum,Har zuwa Kogin Yufiretis.

26. Zai ce mini, ‘Kai ubana ne da Allahna,Kai ne kake kiyaye ni, kai ne Mai Cetona.’

27. Zan maishe shi ɗan farina,Mafi girma daga cikin dukan sarakuna.

28. Zan riƙa ƙaunarsa har abada,Alkawarin da na yi da shi kuma zai tabbata har abada.

29. A kullayaumin daga cikin zuriyarsa ne za a naɗa sarki,Mulkinsa zai dawwama kamar sararin sama.

30. “Amma idan zuriyarsa sun ƙi yin biyayya da shari'ata,Ba su kuwa zauna cikin ka'idodina ba,

31. In sun ƙyale koyarwata,Ba su kiyaye umarnaina ba,

32. To, sai in hukunta su saboda zunubansu,Zan bulale su saboda laifofinsu.

Karanta cikakken babi Zab 89