Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 78:53-59 Littafi Mai Tsarki (HAU)

53. Ya bi da su lafiya, ba su kuwa ji tsoro ba,Amma teku ta cinye abokan gābansu.

54. Ya kawo su tsattsarkar ƙasarsa,Ya kawo su a duwatsun da shi kansa ya ci da yaƙi.

55. Ya kori mazaunan wurin sa'ad da jama'arsa suka dirkako,Ya rarraba ƙasar ga kabilan Isra'ila,A nan ya ba su izini su zauna a wurin, a cikin alfarwansu.

56. Amma sai suka yi wa Allah Mai Iko Dukka tawaye,Suka jarraba shi.Ba su kiyaye dokokinsa ba,

57. Amma suka yi tawaye da rashin aminciKamar kakanninsu,Kamar kiban da aka harba da tanƙwararren baka,Waɗanda ba su da tabbas.

58. Suka sa shi ya yi fushi sabodaMasujadansu na arnanci.Suka sa ya ji kishi saboda gumakansu.

59. Allah ya yi fushi sa'ad da ya ga haka,Don haka ya rabu da jama'arsa ɗungum.

Karanta cikakken babi Zab 78