Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 78:49-56 Littafi Mai Tsarki (HAU)

49. Ya buge su da fushinsa mai zafi, da hasalarsa,Ya sa su damuwa ƙwarai,Da ya aiko da mala'iku masu hallakarwa.

50. Bai kanne fushinsa ba,Bai bar su da rai ba,Amma ya karkashe su da annoba.

51. Ya karkashe 'yan fari mazaNa dukan iyalan da suke Masar.

52. Sa'an nan ya bi da jama'arsaKamar makiyayi, ya fito da su,Ya yi musu jagora cikin hamada.

53. Ya bi da su lafiya, ba su kuwa ji tsoro ba,Amma teku ta cinye abokan gābansu.

54. Ya kawo su tsattsarkar ƙasarsa,Ya kawo su a duwatsun da shi kansa ya ci da yaƙi.

55. Ya kori mazaunan wurin sa'ad da jama'arsa suka dirkako,Ya rarraba ƙasar ga kabilan Isra'ila,A nan ya ba su izini su zauna a wurin, a cikin alfarwansu.

56. Amma sai suka yi wa Allah Mai Iko Dukka tawaye,Suka jarraba shi.Ba su kiyaye dokokinsa ba,

Karanta cikakken babi Zab 78