Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 78:38-52 Littafi Mai Tsarki (HAU)

38. Amma Allah ya yi wa jama'arsa jinƙai,Ya gafarta zunubansu,Bai hallaka su ba.Sau da yawa yakan kanne fushinsa,Ya dakatar da hasalarsa.

39. Yakan tuna su mutane ne kawai,Kamar iskar da take hurawa ta wuce .

40. Sau da yawa suka tayar masa a hamada.Sau da yawa suka sa shi yin ɓacin rai!

41. Suka yi ta jarraba Allah a kai a kai,Suka kuwa sa Mai Tsarki na Isra'ila yin fushi.

42. Suka manta da ikonsa mai girma.Suka manta da lokacin da ya cece su daga abokan gābansu,

43. Lokacin da ya aikata manyan ayyuka da mu'ujizaiA filin Zowan, ta ƙasar Masar.

44. Ya mai da koguna su zama jini,Masarawa kuwa suka kasa sha daga rafuffukansu.

45. Ya aiko da ƙudaje gare su, suka wahalshe su,Kwaɗi suka lalata filayensu.

46. Ya aiko da gamzari don su ci amfanin gonakinsu,Ya aiko da ɗango su lalata gonakinsu.

47. Ya kashe kurangar inabinsu da ƙanƙara,Ya kuma kashe itatuwan ɓaurensu da jaura.

48. Ya karkashe shanunsu da ƙanƙara,Ya kuma karkashe garkunan tumakinsu da na awakinsu da tsawa.

49. Ya buge su da fushinsa mai zafi, da hasalarsa,Ya sa su damuwa ƙwarai,Da ya aiko da mala'iku masu hallakarwa.

50. Bai kanne fushinsa ba,Bai bar su da rai ba,Amma ya karkashe su da annoba.

51. Ya karkashe 'yan fari mazaNa dukan iyalan da suke Masar.

52. Sa'an nan ya bi da jama'arsaKamar makiyayi, ya fito da su,Ya yi musu jagora cikin hamada.

Karanta cikakken babi Zab 78