Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 78:36-44 Littafi Mai Tsarki (HAU)

36. Amma maganganunsu duka ƙarya ne,Dukan abin da suka faɗa kuwa daɗin baki ne kawai.

37. Ba su yi masa biyayya ba,Ba su yi aminci game da alkawarin da suka yi da shi ba.

38. Amma Allah ya yi wa jama'arsa jinƙai,Ya gafarta zunubansu,Bai hallaka su ba.Sau da yawa yakan kanne fushinsa,Ya dakatar da hasalarsa.

39. Yakan tuna su mutane ne kawai,Kamar iskar da take hurawa ta wuce .

40. Sau da yawa suka tayar masa a hamada.Sau da yawa suka sa shi yin ɓacin rai!

41. Suka yi ta jarraba Allah a kai a kai,Suka kuwa sa Mai Tsarki na Isra'ila yin fushi.

42. Suka manta da ikonsa mai girma.Suka manta da lokacin da ya cece su daga abokan gābansu,

43. Lokacin da ya aikata manyan ayyuka da mu'ujizaiA filin Zowan, ta ƙasar Masar.

44. Ya mai da koguna su zama jini,Masarawa kuwa suka kasa sha daga rafuffukansu.

Karanta cikakken babi Zab 78