Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 78:34-42 Littafi Mai Tsarki (HAU)

34. Amma sa'ad da ya kashe waɗansunsu,Sai sauran suka juyo gare shi suka tuba,Suka yi addu'a sosai a gare shi.

35. Sun tuna, ashe, Allah ne mai kiyaye su,Sun tuna Maɗaukaki shi ne Mai Fansarsu.

36. Amma maganganunsu duka ƙarya ne,Dukan abin da suka faɗa kuwa daɗin baki ne kawai.

37. Ba su yi masa biyayya ba,Ba su yi aminci game da alkawarin da suka yi da shi ba.

38. Amma Allah ya yi wa jama'arsa jinƙai,Ya gafarta zunubansu,Bai hallaka su ba.Sau da yawa yakan kanne fushinsa,Ya dakatar da hasalarsa.

39. Yakan tuna su mutane ne kawai,Kamar iskar da take hurawa ta wuce .

40. Sau da yawa suka tayar masa a hamada.Sau da yawa suka sa shi yin ɓacin rai!

41. Suka yi ta jarraba Allah a kai a kai,Suka kuwa sa Mai Tsarki na Isra'ila yin fushi.

42. Suka manta da ikonsa mai girma.Suka manta da lokacin da ya cece su daga abokan gābansu,

Karanta cikakken babi Zab 78