Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 78:22-38 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. Saboda ba su amince da shi ba,Ba su kuma gaskata yana da ikon cetonsu ba.

23. Amma ya yi magana da sararin sama,Ya umarci ƙofofinsa su buɗe,

24. Ya ba su tsaba daga sama,Da ya sauko musu da manna, su ci.

25. Ta haka suka ci abincin mala'iku.Allah ya ba su iyakar abin da za su iya ci.

26. Sa'an nan sai ya sa iskar gabas ta hura,Da ikonsa kuma ya sa iskar kudu ta tashi.

27. Ya aika da tsuntsaye bisansu kamar ƙura,Yawansu kamar yashi a gaɓa,

28. Sai suka fāɗo a zango,Kewaye da alfarwai ko'ina.

29. Sai mutane suka ci suka ƙoshi,Allah ya ba su iyakar abin da suke bukata.

30. Amma sa'ad da suke cikin ci,Tun ba su ƙoshi ba,

31. Sai Allah ya yi fushi da su.Ya karkashe ƙarfafan mutane,Da samarin Isra'ila na gaske!

32. Ko da yake ya aikata mu'ujizai da yawa,Duk da haka jama'a suka ci gaba da yin zunubi,Ba su kuwa gaskata shi ba.

33. Ta haka ya ƙare kwanakinsu kamar fitar numfashi,Bala'i ya aukar wa rayukansu farat ɗaya.

34. Amma sa'ad da ya kashe waɗansunsu,Sai sauran suka juyo gare shi suka tuba,Suka yi addu'a sosai a gare shi.

35. Sun tuna, ashe, Allah ne mai kiyaye su,Sun tuna Maɗaukaki shi ne Mai Fansarsu.

36. Amma maganganunsu duka ƙarya ne,Dukan abin da suka faɗa kuwa daɗin baki ne kawai.

37. Ba su yi masa biyayya ba,Ba su yi aminci game da alkawarin da suka yi da shi ba.

38. Amma Allah ya yi wa jama'arsa jinƙai,Ya gafarta zunubansu,Bai hallaka su ba.Sau da yawa yakan kanne fushinsa,Ya dakatar da hasalarsa.

Karanta cikakken babi Zab 78