Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 78:20-30 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. Gaskiya ce, ya bugi dutse,Ruwa kuwa ya fito a yalwace,Amma ko yana da iko ya ba da abinci da nama ga jama'arsa?”

21. Saboda haka Allah ya yi fushi sa'ad da ya ji su,Ya aukar wa jama'arsa da wuta,Fushinsa ya haɓaka a kansu,

22. Saboda ba su amince da shi ba,Ba su kuma gaskata yana da ikon cetonsu ba.

23. Amma ya yi magana da sararin sama,Ya umarci ƙofofinsa su buɗe,

24. Ya ba su tsaba daga sama,Da ya sauko musu da manna, su ci.

25. Ta haka suka ci abincin mala'iku.Allah ya ba su iyakar abin da za su iya ci.

26. Sa'an nan sai ya sa iskar gabas ta hura,Da ikonsa kuma ya sa iskar kudu ta tashi.

27. Ya aika da tsuntsaye bisansu kamar ƙura,Yawansu kamar yashi a gaɓa,

28. Sai suka fāɗo a zango,Kewaye da alfarwai ko'ina.

29. Sai mutane suka ci suka ƙoshi,Allah ya ba su iyakar abin da suke bukata.

30. Amma sa'ad da suke cikin ci,Tun ba su ƙoshi ba,

Karanta cikakken babi Zab 78