8. Zai hallaka su saboda maganganunsu,Duk wanda ya gan su zai kaɗa kansa.
9. Dukansu za su ji tsoro,Za su faɗi abin da Allah ya aikata,Su yi tunani a kan ayyukansa.
10. Dukan masu adalci za su yi murna,Saboda abin da Ubangiji ya aikata.Za su sami mafaka a gare shi,Dukan mutanen kirki za su yabe shi.