Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 60:6-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. A tsattsarkan wurinsa, Allah ya faɗa ya ce,“Da nasara zan raba Shekem,Da nasara kuma zan rarraba Sukkot ga jama'ata.

7. Gileyad tawa ce, har da Manassa ma,Ifraimu ne kwalkwalina,Yahuza kuma sandana ne na sarauta.

8. Amma zan yi amfani da Mowab kamar kwanon wanki,Edom kuwa kamar akwatin takalmina.Zan yi sowar nasara a kan Filistiyawa.”

9. Ya Allah, wa zai kai ni birni mai kagara?Wa zai kai ni Edom?

10. Da gaske ka yashe mu ke nan?Ba za ka yi tafiya tare da sojojinmu ba?

11. Ka taimake mu, mu yaƙi abokan gāba,Domin taimako irin na mutum banza ne!

12. Idan Allah yana wajenmu,Za mu yi nasara,Zai kori abokan gābanmu.

Karanta cikakken babi Zab 60