7. Ka hukunta su, ya Allah saboda muguntarsu,Da fushinka ka kori waɗannan mutane!
8. Ka san irin wahalar da nake sha,Kana riƙe da lissafin yawan hawayena.Ashe, ba a rubuce suke a littafinka ba?
9. A ranar da na yi kira gare ka,Za a komar da abokan gābana baya,Gama na sani Allah yana tare da ni!
10. Ina dogara ga Allah, ina yabon alkawarinsa,Ina dogara ga Ubangiji, ina yabon alkawarinsa.