Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 55:19-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

19. Allah, shi wanda yake mulki tun fil azal,Zai ji ni, zai kore su.Ba abin da suka iya yi a kai,Domin ba su tsoron Allah.

20. Abokina na dā,Ya yi wa abokansa faɗa,Ya ta da alkawarinsa.

21. Kalmominsa sun fi mai taushi,Amma ƙiyayya tana a zuciyarsa,Kalmominsa sun fi mai sulɓi,Amma suna yanka kamar kakkaifan takobi.

22. Ka gabatar da wahalarka ga Ubangiji,Zai kuwa taimake ka,Ba zai bari a ci nasara a kan mutumin kirki ba, faufau.

23. Amma kai, ya Allah, za ka jefar da masu kisankai, da maƙaryata can ƙasa cikin zurfafa,Kafin su kai rabin kwanakinsu a duniya.Amma ni, zan dogara gare ka.

Karanta cikakken babi Zab 55