12. Da a ce maƙiyina ne yake mini ba'a,Da sai in jure.Da a ce abokin gābana ne yake shugabancina,Da sai in ɓuya masa.
13. Amma kai ne, aminina,Abokin aikina ne, abokina ne kuma!
14. Dā mukan yi taɗi da juna ƙwarai,Mukan tafi Haikali tare da sauran jama'a.
15. Allah ya sa mutuwa ta auko wa maƙiyana ba labari,Allah ya sa su gangara ƙasar matattu da ransu!Mugunta tana cikin gidajensu da zukatansu.