Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 46:5-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Allah yana zaune cikin birnin,Ba kuwa za a hallaka birnin ba, faufau.Da asuba Allah zai kawo musu gudunmawa.

6. An kaɓantar da sauran al'umma, mulkoki suka girgiza,Allah ya yi tsawa, duniya kuwa ta narke.

7. Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu,Allah na Yakubu shi ne mafakarmu!

8. Zo ku ga abin da Ubangiji ya yi!Dubi irin ayyukan al'ajabi da ya yi a duniya!

9. Ya hana yaƙoƙi ko'ina a duniya,Yana karya bakkuna, yana lalatar da māsu,Yana ƙone karusai da wuta.

10. Ya ce, “Ku yi shiru, ku sani ni ne Allah,Maɗaukaki ne cikin sauran al'umma,Maɗaukaki kuma a duniya!”

11. Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu,Allah na Yakubu shi ne mafakarmu!

Karanta cikakken babi Zab 46