Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 46:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Allah ne mafakarmu da ƙarfinmu,Kullum a shirye yake yă yi taimako a lokacin wahala.

2. Saboda haka ba za mu ji tsoro ba,Ko da duniya za ta girgiza,Duwatsu kuma su fāɗa cikin zurfafan teku,

3. Ko da a ce tekuna za su yi ruri su tumbatsa,Tuddai kuma su girgiza saboda tangaɗin tekun.

4. Akwai kogin da yake kawo farin ciki a birnin Allah,Da cikin tsattsarkan Haikali na Maɗaukaki.

Karanta cikakken babi Zab 46