Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 3:1-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ina da maƙiya da yawa, ya Ubangiji,Da yawa kuma sun juya, suna gāba da ni!

2. Suna magana a kaina, suna cewa,“Allah ba zai taimake shi ba!”

3. Amma kai, ya Ubangiji, kullum kana kiyaye ni daga hatsari,Kana ba ni nasara,Kana kuma maido mini da ƙarfin halina.

4. Na yi kira wurin Ubangiji domin taimako,Ya kuwa amsa mini daga tsattsarkan dutsensa.

5. Na kwanta na yi barci,Na kuwa tashi lafiya lau,Gama Ubangiji yana kiyaye ni.

6. Ba na jin tsoron dubban abokan gābaWaɗanda suka kewaye ni ta kowane gefe.

7. Ka zo, ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna!Ka yi nasara a kan dukan abokan gābana,Ka hallakar da dukan mugaye.

8. Ceto yana zuwa daga wurin Ubangiji,Bari yă sa wa jama'arsa albarka!

Karanta cikakken babi Zab 3