Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 26:4-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Ba na tarayya da mutanen banza,Ba abin da ya gama ni da masu riya.

5. Ina ƙin tarayya da masu mugunta,Nakan kauce wa mugaye.

6. Ya Ubangiji, na wanke hannuwanaDon in nuna ba ni da laifi,Da ibada nakan taka, ina kewaya bagadenka.

7. Na raira waƙar godiya,Na faɗi dukan ayyukanka masu banmamaki.

8. Ya Ubangiji, ina ƙaunar Haikali inda zatinka yake,Inda ɗaukakarka yake zaune.

9. Kada ka hallaka ni tare da masu zunubi,Ka cece ni daga ƙaddarar masu kisankai,

10. Mutanen da suke aikata mugunta a dukan lokaci,A koyaushe suna shirye don su ba da rashawa.

11. Amma ni, ina yin abin da yake daidai,Ka yi mini jinƙai ka fanshe ni!

12. Na kuɓuta daga dukan hatsarori,A taron sujada na yabi Ubangiji!

Karanta cikakken babi Zab 26