14. Ubangiji yakan amince da waɗanda suke biyayya da shi,Yakan koya musu alkawarinsa.
15. A koyaushe ga Ubangiji nake neman taimako,Yakan kuɓutar da ni daga hatsari.
16. Ka juyo wajena, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai,Gama ina zaman kaɗaici da rashin ƙarfi.
17. Damuwar zuciyata ta yi yawa,Ka raba ni da dukan damuwa,Ka cece ni daga dukan wahalata.
18. Ka kula da wahalata da azabata,Ka gafarta dukan zunubaina.