Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 18:5-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Mutuwa ta ɗaure ni kam da igiyoyinta,Kabari kuma ya ɗana mini tarko.

6. A shan wahalata na kira ga Ubangiji,Na yi kira ga Allahna domin neman taimako.A Haikalinsa ya ji muryata,Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.

7. Sai duniya ta raurawa ta girgiza,Harsashin duwatsu suka jijjigu, suka girgizaSaboda Allah ya husata!

8. Hayaƙi ya yi ta tuƙaƙowa daga hancinsa,Harshen wuta da garwashi suna fitowa daga bakinsa.

9. Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa,Tare da girgije mai duhu a ƙarƙashin ƙafafunsa.

10. Ya sauko ta bisa bayan kerubobi,Yana tafe da sauri a kan fikafikan iska.

11. Ya rufe kansa da duhu,Gizagizai masu duhu cike da ruwa, suna kewaye da shi.

12. Ƙanƙara da garwashin wuta suka saukoDaga cikin walƙiya da take gabansa,Suka keto ta cikin gizagizai masu duhu.

13. Sa'an nan Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama,Aka ji muryar Maɗaukaki.Ƙanƙara da garwashin wuta suka sauko.

14. Ya harba kibansa, ya watsa magabtana,Da walƙatawar walƙiya ya kore su.

15. Kashiyar teku ta bayyana,Tussan duniya sun bayyana,Sa'ad da ka tsauta wa magabtana, ya Ubangiji,Sa'ad da kuma ka yi musu tsawa da fushi.

Karanta cikakken babi Zab 18