Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 18:41-46 Littafi Mai Tsarki (HAU)

41. Suna kukan neman taimako, amma ba wanda zai iya cetonsu,Za su yi kira ga Ubangiji, amma ba zai amsa ba.

42. Zan murƙushe su har su zama ƙuraWadda iska take kwashewa,Zan tattake su kamar caɓi a titi.

43. Ka cece ni daga mutane masu tawaye,Ka naɗa ni in yi mulkin sauran al'umma,Jama'ar da ban san ta ba, ta zama abin mulkina.

44. Za su yi biyayya sa'ad da suka ji ni,Baƙi za su rusuna mini,

45. Za su karai,Su fita, suna rawar jiki daga kagaransu.

46. Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga mai kāre ni!Allah ne, Mai Cetona! A yi shelar girmansa!

Karanta cikakken babi Zab 18