Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 18:28-45 Littafi Mai Tsarki (HAU)

28. Ubangiji yakan ba ni haske,Allah yakan kawar da duhuna.

29. Yakan ba ni ƙarfin da zan fāɗa wa magabtana,Da ikon rinjayar kagararsu.

30. Wannan Allah dai! Ayyukansa kamiltattu ne ƙwarai,Maganarsa abar dogara ce!Kamar garkuwa yake, ga duk mai neman taimako a wurinsa.

31. Ubangiji shi kaɗai ne Allah,Allah ne kaɗai kāriyamu.

32. Shi ne Allahn da yake ƙarfafa ni,Yana kiyaye lafiyata a kan hanya.

33. Yana sa in tabbata lafiya nake tafiya, kamar barewa.Yana kiyaye ni lafiya a kan duwatsu.

34. Yakan horar da ni don yaƙi,Domin in iya amfani da baka mafi ƙarfi.

35. Ya Ubangiji ka kiyaye ni, ka cece ni,Na zama babban mutum saboda kana lura da ni,Ikonka kuma ya kiyaye lafiyata.

36. Ka tsare ni, ba a kama ni ba,Ban kuwa taɓa fāɗuwa ba.

37. Na kori magabtana, har na kama su,Ba zan tsaya ba, sai na yi nasara da su.

38. Zan buge su har ƙasa, ba kuwa za su tashi ba,Za su fāɗi ƙarƙashin ƙafafuna.

39. Kakan ba ni ƙarfin yin yaƙi,Kakan ba ni nasara a kan magabtana.

40. Ka kori magabtana daga gare ni,Zan hallaka waɗanda suke ƙina.

41. Suna kukan neman taimako, amma ba wanda zai iya cetonsu,Za su yi kira ga Ubangiji, amma ba zai amsa ba.

42. Zan murƙushe su har su zama ƙuraWadda iska take kwashewa,Zan tattake su kamar caɓi a titi.

43. Ka cece ni daga mutane masu tawaye,Ka naɗa ni in yi mulkin sauran al'umma,Jama'ar da ban san ta ba, ta zama abin mulkina.

44. Za su yi biyayya sa'ad da suka ji ni,Baƙi za su rusuna mini,

45. Za su karai,Su fita, suna rawar jiki daga kagaransu.

Karanta cikakken babi Zab 18