Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 18:27-32 Littafi Mai Tsarki (HAU)

27. Kakan ceci masu tawali'u,Amma kakan ƙasƙantar da masu girmankai.

28. Ubangiji yakan ba ni haske,Allah yakan kawar da duhuna.

29. Yakan ba ni ƙarfin da zan fāɗa wa magabtana,Da ikon rinjayar kagararsu.

30. Wannan Allah dai! Ayyukansa kamiltattu ne ƙwarai,Maganarsa abar dogara ce!Kamar garkuwa yake, ga duk mai neman taimako a wurinsa.

31. Ubangiji shi kaɗai ne Allah,Allah ne kaɗai kāriyamu.

32. Shi ne Allahn da yake ƙarfafa ni,Yana kiyaye lafiyata a kan hanya.

Karanta cikakken babi Zab 18