Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 18:16-31 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Ubangiji ya miƙa hannunsa daga samaniya ya ɗauke ni,Ya tsamo ni daga cikin ruwa mai zurfi.

17. Ya cece ni daga magabtana masu ƙarfi,Daga kuma dukan masu ƙina,Gama sun fi ƙarfina!

18. Sa'ad da nake shan wahala suka auka mini,Amma Ubangiji ya kiyaye ni.

19. Ya fisshe ni daga cikin hatsari,Ya cece ni, don yana jin daɗina.

20. Ubangiji yakan sāka mini, saboda ni adali ne,Yakan sa mini albarka, don ni marar laifi ne.

21. Na yi biyayya da umarnan Ubangiji,Ban yi wa Ubangiji Allahna tawaye ba.

22. Na kiyaye dukan dokokinsa,Ban yi rashin biyayya da umarnansa ba.

23. Ya sani ba ni da laifi,Domin na kiyaye kaina daga mugunta.

24. Don haka ya sāka mini, domin ni adali ne,Gama ya sani ni marar laifi ne.

25. Kai, ya Ubangiji, mai aminci ne ga masu aminci,Kai nagari ne, cikakke ga kamilai.

26. Kai Mai Tsarki ne ga waɗanda suke tsarkaka,Amma kana gāba da mugaye.

27. Kakan ceci masu tawali'u,Amma kakan ƙasƙantar da masu girmankai.

28. Ubangiji yakan ba ni haske,Allah yakan kawar da duhuna.

29. Yakan ba ni ƙarfin da zan fāɗa wa magabtana,Da ikon rinjayar kagararsu.

30. Wannan Allah dai! Ayyukansa kamiltattu ne ƙwarai,Maganarsa abar dogara ce!Kamar garkuwa yake, ga duk mai neman taimako a wurinsa.

31. Ubangiji shi kaɗai ne Allah,Allah ne kaɗai kāriyamu.

Karanta cikakken babi Zab 18