Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 18:13-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Sa'an nan Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama,Aka ji muryar Maɗaukaki.Ƙanƙara da garwashin wuta suka sauko.

14. Ya harba kibansa, ya watsa magabtana,Da walƙatawar walƙiya ya kore su.

15. Kashiyar teku ta bayyana,Tussan duniya sun bayyana,Sa'ad da ka tsauta wa magabtana, ya Ubangiji,Sa'ad da kuma ka yi musu tsawa da fushi.

16. Ubangiji ya miƙa hannunsa daga samaniya ya ɗauke ni,Ya tsamo ni daga cikin ruwa mai zurfi.

17. Ya cece ni daga magabtana masu ƙarfi,Daga kuma dukan masu ƙina,Gama sun fi ƙarfina!

Karanta cikakken babi Zab 18