1. Ina kira ga Ubangiji don neman taimako,Ina roƙonsa.
2. Na kawo masa dukan koke-kokena,Na faɗa masa dukan wahalaina.
3. Sa'ad da na yi niyyar fid da zuciya,Ya san abin da zan yi.A kan hanyar da zan biMaƙiyana sun kafa mini tarko a ɓoye.
4. Na duba kewaye da ni, sai na ga ba ni da wanda zai taimake ni,Ba wanda zai kiyaye ni,Ba kuwa wanda ya kula da ni.