Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 122:1-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Na yi murna sa'ad da suka ce mini,“Tashi mu tafi Haikalin Ubangiji!”

2. Ga shi kuwa, mun iso,Muna tsaye a ƙofofin Urushalima!

3. Urushalima birni ce wadda aka maido ta yadda take dā,Da kyakkyawan tsari, a shirye!

4. A nan kabilai sukan zo,Kabilan Isra'ila,Domin su yi godiya ga Ubangiji,Kamar yadda ya umarce su.

5. A nan majalisu suke,Wurin da sarki yake yi wa jama'arsa shari'a.

6. Ku yi wa Urushalima addu'ar salama!“Allah ya sa masu ƙaunarki su arzuta!

7. Salama ta samu a garukanki,Da zaman lafiya kuma a fādodinki.”

Karanta cikakken babi Zab 122