Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 119:79-91 Littafi Mai Tsarki (HAU)

79. Ka sa waɗanda suke tsoronka su zo gare ni,Da waɗanda suka san umarnanka.

80. Ka sa in yi cikakkiyar biyayya da umarnanka,Sa'an nan zan tsere wa shan kunyar faɗuwa.

81. Na tafke, ya Ubangiji, jira nake ka cece ni,Na dogara ga maganarka.

82. Idanuna sun gaji da zuba ido ga alkawarinka.Roƙo nake, “Sai yaushe za ka taimake ni?”

83. Na zama marar amfani kamar salkar ruwan inabi wanda aka jefar da ita,Duk da haka ban manta da umarnanka ba.

84. Har yaushe zan yi ta jira?Yaushe za ka yi wa waɗanda suke tsananta mini hukunci?

85. Masu girmankai, waɗanda ba su biyayya da dokarka,Sun haƙa wushefe don su kama ni.

86. Umarnanka duka, abin dogara ne,Mutane suna tsananta mini da ƙarairayi,Ka taimake ni!

87. Sun kusa ci wa burinsu na su kashe ni,Amma ban raina ka'idodinka ba.

88. Saboda madawwamiyar ƙaunarka, ka yi mini alheri,Domin in yi biyayya da dokokinka.

89. Maganarka tabbatacciya ce, ya Ubangiji,A kafe take a Sama.

90. Amincinka ya tabbata har abada,Ka kafa duniya a inda take, tana nan kuwa a wurin.

91. Dukan abubuwa suna nan har wa yau saboda umarninka,Domin su duka bayinka ne.

Karanta cikakken babi Zab 119