Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 119:69-87 Littafi Mai Tsarki (HAU)

69. Masu girmankai sun faɗi ƙarairayi a kaina,Amma da zuciya ɗaya nake biyayya da ka'idodinka.

70. Waɗannan mutane ba su da ganewa,Amma ni ina murna da dokarka.

71. Horon da aka yi mini ya yi kyau,Domin ya sa na koyi umarnanka.

72. Dokar da ka yiMuhimmiya ce a gare ni,Fiye da dukan dukiyar duniya.

73. Kai ne ka halicce ni, ka kuma kiyaye ni lafiya,Ka ba ni ganewa, don in koyi dokokinka.

74. Waɗanda suke tsoronka za su yi murna sa'ad da suka gan ni,Saboda ina dogara ga alkawarinka.

75. Na sani ka'idodinka na adalci ne, ya Ubangiji,Ka hore ni, domin kai mai aminci ne.

76. Ka sa madawwamiyar ƙaunarka ta ta'azantar da ni,Kamar yadda ka alkawarta mini, ni bawanka.

77. Ka yi mini jinƙai, zan rayu,Saboda ina murna da dokarka.

78. Ka kunyatar da masu girmankaiSaboda sun ba da shaidar zur a kaina,Amma ni, zan yi tunani a kan ka'idodinka.

79. Ka sa waɗanda suke tsoronka su zo gare ni,Da waɗanda suka san umarnanka.

80. Ka sa in yi cikakkiyar biyayya da umarnanka,Sa'an nan zan tsere wa shan kunyar faɗuwa.

81. Na tafke, ya Ubangiji, jira nake ka cece ni,Na dogara ga maganarka.

82. Idanuna sun gaji da zuba ido ga alkawarinka.Roƙo nake, “Sai yaushe za ka taimake ni?”

83. Na zama marar amfani kamar salkar ruwan inabi wanda aka jefar da ita,Duk da haka ban manta da umarnanka ba.

84. Har yaushe zan yi ta jira?Yaushe za ka yi wa waɗanda suke tsananta mini hukunci?

85. Masu girmankai, waɗanda ba su biyayya da dokarka,Sun haƙa wushefe don su kama ni.

86. Umarnanka duka, abin dogara ne,Mutane suna tsananta mini da ƙarairayi,Ka taimake ni!

87. Sun kusa ci wa burinsu na su kashe ni,Amma ban raina ka'idodinka ba.

Karanta cikakken babi Zab 119