10. Da zuciya ɗaya nake ƙoƙarin bauta maka,Ka kiyaye ni daga rashin biyayya da umarnanka!
11. Na riƙe maganarka a zuciyata,Don kada in yi maka zunubi.
12. Ina yabonka, Ya Ubangiji,Ka koya mini ka'idodinka!
13. Zan ta da murya,In maimaita dukan dokokin da ka bayar.
14. Ina murna da bin umarnanka,Fiye da samun dukiya mai yawa.
15. Nakan yi nazarin umarnanka,Nakan kuma yi bimbinin koyarwarka.