Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 106:7-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Kakanninmu a MasarBa su fahimci ayyukan Allah masu banmamaki ba,Sau da yawa sukan manta da irin ƙaunar da ya nuna musu,Suka tayar wa Mai Iko Dukka a Bahar Maliya.

8. Amma duk da haka ya cece su, kamar yadda ya alkawarta,Domin ya nuna ikonsa mai girma.

9. Ya tsauta wa Bahar Maliya, ta ƙafe,Har ya bi da jama'arsa su hayeKamar a bisa busasshiyar ƙasa.

10. Ya cece su daga maƙiyansu,Ya ƙwato su daga wurin abokan gābansu.

11. Ruwa ya cinye maƙiyansu,Ba wanda ya tsira.

12. Sa'an nan jama'arsa suka gaskata alkawarinsa,Suka raira yabo gare shi.

13. Amma nan da nan, suka manta da abin da ya yi,Suka aikata, ba su jira shawararsa ba.

14. Suka cika da sha'awa cikin hamada,Suka jarraba Allah,

15. Sai ya ba su abin da suka roƙa,Amma ya aukar musu da muguwar cuta.

16. Can cikin hamada suka ji kishin MusaDa Haruna, bayin Ubangiji, tsarkaka,

17. Sai ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan,Ta binne Abiram da iyalinsa.

18. Wuta ta sauko bisa magoya bayansu,Ta ƙone mugayen mutanen nan.

19. Suka ƙera ɗan maraƙi da zinariya a Horeb,Suka yi masa sujada.

20. Suka musaya ɗaukakar AllahDa siffar dabba mai cin ciyawa.

21. Suka manta da Allah wanda ya cece su,Ta wurin manyan ayyuka da ya yi a Masar.

22. Kai, Allah ya aikata abubuwa masu ban al'ajabi a can!Ga kuma abubuwa masu banmamaki da ya aikata a Bahar Maliya!

23. Saboda wannan Allah ya ce zai hallaka jama'arsa,Amma Musa, zaɓaɓɓen bawansa, ya yi godo ga Allah,Allah kuwa ya huce, bai hallaka su ba.

Karanta cikakken babi Zab 106