18. Wuta ta sauko bisa magoya bayansu,Ta ƙone mugayen mutanen nan.
19. Suka ƙera ɗan maraƙi da zinariya a Horeb,Suka yi masa sujada.
20. Suka musaya ɗaukakar AllahDa siffar dabba mai cin ciyawa.
21. Suka manta da Allah wanda ya cece su,Ta wurin manyan ayyuka da ya yi a Masar.
22. Kai, Allah ya aikata abubuwa masu ban al'ajabi a can!Ga kuma abubuwa masu banmamaki da ya aikata a Bahar Maliya!