Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yush 9:12-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

12. Ko sun goyi 'ya'ya,Zan sa su mutu tun ba su balaga ba.Tasu ta ƙare sa'ad da na rabu da su!”

13. Ya Ubangiji, na ga yadda IfraimuTa mai da 'ya'yanta ganimaTana fitar da su zuwa wurin yanka.

14. Ya Ubangiji, me zan ce ka ba su?Me za ka ba su?Ka ba su cikin da ba ya haihuwa da busassun mama.

15. Ubangiji ya ce, “Kowace irin muguntarsu tana a Gilgal,A can na ƙi su!Saboda mugayen ayyukansu, zan kore su daga ƙasata,Ba kuma zan ƙaunace su ba.Dukan shugabanninsu 'yan tayarwa ne.

16. An ka da mutanen Ifraimu, saiwarsu ta bushe.Ba za su yi 'ya'ya ba.Ko ma sun haihu, zan kashe 'ya'yan nan nasu waɗanda suke ƙauna.”

17. Allahna zai ƙi suDomin ba su yi masa biyayya ba.Za su zama masu yawo cikin al'ummai.

Karanta cikakken babi Yush 9