Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yush 7:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. “Sa'ad da zan warkar da mutanen Isra'ila,Sai zunubin Ifraimu da muguntar Samariya su bayyana,Gama suna cin amana.Ɓarawo yakan fasa, ya shiga,'Yan fashi suna fashi a fili,

2. Amma ba su tunani,Cewa zan tuna da dukan muguntarsu.Yanzu ayyukansu sun kewaye su,Ina ganinsu.

3. “Suna faranta zuciyar sarki da muguntarsu,Na shugabanni kuma da ƙarairayinsu.

4. Dukansu mazinata ne,Suna kama da tanda da aka zafafa,Wadda matoyi ya daina iza mata wuta,Tun daga lokacin cuɗe kulluHar zuwa lokacin da yisti ya tasar da shi.

Karanta cikakken babi Yush 7