1. Ya ku mutanen Isra'ila, ku ji maganar Ubangiji,Gama Ubangiji yana da shari'a da ku, ku mazaunan ƙasar.“Gama ba gaskiya, ko ƙauna,Ko sanin Ubangiji a ƙasar.
2. Akwai rantsuwa, da ƙarya, da kisankai, da sata, da zina,Da kama-karya, da zub da jini a kai a kai.
3. Saboda haka ƙasar za ta yi makoki,Dukan waɗanda yake zaune a cikinta za su yi yaushi.Namomin jeji kuma, da tsuntsaye, da kifaye za su ƙare.
4. “Duk da haka kada wani ya sa wa mutum laifi,Kada wani kuma ya tsautar.Da ku nake magana, ku firistoci.