Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Rut 3:5-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Rut ta amsa, “Zan yi dukan abin da kika faɗa.”

6. Rut kuwa ta gangara zuwa masussukar, ta yi yadda surukarta ta faɗa mata.

7. Sa'ad da Bo'aza ya ci ya sha yana cikin jin daɗi, sai ya je ya kwanta kusa da tsibin tsabar sha'ir. Sa'an nan Rut ta tafi a hankali, ta buɗe mayafin da ya rufa da shi wajen ƙafafunsa, ta kwanta a ciki.

8. Da tsakar dare, sai mutumin ya farka a firgice, ya juya, sai ga mace kwance a wajen ƙafafunsa.

9. Ya ce, “Wace ce?”Sai ta amsa, “Ni ce Rut, baranyarka, sai ka rufe ni da mayafinka, gama kai dangi ne na kusa.”

10. Sa'an nan ya ce, “Ubangiji ya sa miki albarka 'yata, yanzu kin nuna alheri mafi girma fiye da na dā da yake ba ki nemi saurayi, matalauci ko attajiri ba.

11. Yanzu dai, 'yata, kada ki damu, zan yi miki dukan abin da kika roƙa, gama dukan mutanen garin sun sani ke macen kirki ce.

Karanta cikakken babi Rut 3