Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Neh 9:31-38 Littafi Mai Tsarki (HAU)

31. Duk da haka, saboda yawan jinƙanka,Ba ka yashe su ko ka hallaka su ba.Kai Allah mai alheri ne mai jinƙai!

32. “Ya Allah, Allahnmu, da girma kake!Kai mai banrazana ne, cike da iko!Da aminci ka cika alkawaranka da ka alkawarta.Daga lokacin da Sarkin Assuriya ya danne mu,Har yanzu ma, wace wahala ce ba mu sha ba!Sarakunanmu, da shugabanninmu, da firistocinmu,Da annabawanmu, da kakanninmu,Da dukan sauran jama'arka sun sha wahala.Ka san irin wahalar da muka sha.

33. Ka yi daidai da ka hukunta mu haka!Kai mai aminci ne, mu kuwa mun yi zunubi.

34. Gama kakanninmu, da sarakunanmu,Da shugabanninmu, da firistocinmu,Ba su kiyaye dokarka ba.Ba su kasakunne ga umarnanka da gargaɗinka ba.Da waɗannan ne kake zarginsu.

35. Da albarkacinka sarakuna suke mulkin jama'arka,Sa'ad da suke ƙasashen waje, ƙasa mai dausayi ka ba su,Amma ba su juyo su bar zunubi, su bauta maka ba.

36. Ga shi, a yau mu bayi ne a ƙasar da ka ba mu,Wannan ƙasa mai dausayi wadda take ba mu abinci.

37. Amfanin ƙasa duk yana tafiya ga sarakunanDa ka ɗora su a kanmu saboda mun yi zunubi.Suna yi mana yadda suka ga dama, mu da dabbobinmu,Muna cikin baƙin ciki.”

38. “Saboda wannan duka muke yin alkawari mai ƙarfi a rubuce. Shugabanninmu kuwa, da Lawiyawanmu, da firistocinmu, suka buga hatimi, suka sa hannu.”

Karanta cikakken babi Neh 9