Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Neh 1:8-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Ka tuna da maganar da ka umarci bawanka Musa cewa, ‘Idan kun yi rashin aminci, zan warwatsa ku cikin al'ummai.

9. Amma idan kun juyo wurina, kun kiyaye umarnaina, kun aikata su, ko da yake an warsatsar da ku can nesa, zan tattaro ku, in kawo ku wurin da na zaɓa domin in sa sunana ya kahu a wurin.’

10. “Su bayinka ne, mutanenka ne kuma, waɗanda ka fansa da ikonka.

11. Ya Ubangiji, ka kasa kunne ga addu'ar bawanka, da addu'o'in bayinka, waɗanda suke jin daɗin girmama sunanka. Ka ba bawanka nasara yau ka sa ya sami tagomashi a gaban mutumin nan.”

Karanta cikakken babi Neh 1