Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Nah 3:10-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Duk da haka an tafi da ita, an kai tacikin bauta.An fyaɗa ƙanananta a ƙasa,An yi kacakaca da su a kowacemararraba.An jefa kuri'a a kan manyanmutanenta,Aka ɗaure dukan manyan mutanentada sarƙoƙi.

11. Ke Nineba kuma za ki bugu,Za a ɓoye ki.Za ki nemi mafaka a wurin maƙiyinki.

12. Dukan kagaranki suna kama daitatuwan ɓaure,Waɗanda 'ya'yansu suka harba.Da an girgiza sai su faɗo a bakin maisha.

13. Sojojinki kamar mata suke atsakiyarki!An buɗe wa maƙiyanki ƙofofinƙasarki.Wuta za ta cinye madogaranƙofofinki.

14. Ki tanada ruwa domin za a kewayeki da yaƙi!Ki ƙara ƙarfin kagaranki!Ki tafi kududdufi, ki kwaɓa laka!Ki ɗauki abin yin tubali!

15. A can wuta za ta cinye ki,Takobi zai sare ki,Zai cinye ki kamar fara.Ki riɓaɓɓanya kamar fara.Ki kuma riɓaɓɓanya kamar ɗango.

16. Kin yawaita 'yan kasuwanki suna dayawa fiye da taurari,Amma sun tafi kamar fara waɗandasukan buɗe fikafikansu su tashi, sutafi.

17. Shugabanninki kamar ɗango suke,Manyan mutanenki kamarcincirindon fāra ne,Suna zaune a kan shinge a kwanakinsanyi,Sa'ad da rana ta fito, sukan tashi sutafi,Ba wanda ya san inda suke.

18. Ya Sarkin Assuriya, masu tsaronkasuna barci,Manyan mutanenka sunakwankwance,Mutanenka sun watse cikinduwatsu,Ba wanda zai tattaro su.

19. Ba abin da zai rage zafin rauninka,Rauninka ba ya warkuwa.Duk wanda ya ji labarinka, zai tafahannuwansaGama wane ne ba ka musguna waba?

Karanta cikakken babi Nah 3