Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mika 6:1-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. “Ku ji abin da ni Ubangijinake cewa,Tashi ku gabatar da ƙararku agaban duwatsu,Ku bar tuddai su ji muryarku.

2. “Ku duwatsu da madawwaman tussanduniya,Ku ji tuhumar da Ubangiji yake yimuku.Gama Ubangiji, yana da maganagāba da mutanensa,Zai tuhumi Isra'ila.

3. “Ya ku jama'ata, me na yi muku?Wace irin fitina nake yi muku?Ku amsa mini!

4. Gama na fito da ku daga ƙasarMasar,Na fanshe ku daga gidan bauta.Na aika muku da Musa, da Haruna,da Maryamu.

5. Ya ku jama'ata, ku tunaDa abin da Balak, Sarkin Mowab, yaƙulla,Da yadda Bal'amu ɗan Beyor yaamsa masa,Da abin da ya faru daga Shittim, harzuwa Gilgal,Don ku san ayyukan adalci naUbangiji.”

6. Da me zan zo gaban Ubangiji,In sunkuyar da kaina a gaban Allahna Sama?Ko in zo gabansa da maraƙi banaɗaya domin yin hadaya taƙonawa?

7. Ubangiji zai yi murna da ragunadubbaiKo kuwa da kogunan mai dubbai?Zan ba da ɗan farina ne donlaifina?Ko kuwa zan ba da 'ya'yana sabodazunubina?

8. Ya kai mutum, ya riga ya nunamaka abin da yake mai kyau.Abin da Ubangiji yake so gare ka,shi neKa yi adalci, ka ƙaunaci aikataalheri,Ka bi Allah da tawali'u.

9. Ubangiji yana kira ga birnin.Hikima ce ƙwarai a ji tsoronsunanka.“Ki ji ya kabila, wa ya sa mikilokacinki?

10. Ba zan manta da dukiya ta muguntaa gidan mugu ba,Ba kuwa zan manta da bugaggenmudun awo ba.

Karanta cikakken babi Mika 6