Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mika 3:4-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Sa'an nan za su yi kuka ga Ubangiji,Amma Ubangiji ba zai amsa musuba.Zai ɓoye musu fuskarsa a wannanlokaci,Saboda mugayen ayyukansu.

5. Ga abin da Ubangiji ya ce a kanannabawan da suka bi damutanensa a karkace,Waɗanda suke cewa, “Salama,”sa'ad da suke da abinci,Amma sukan kai yaƙin shahadaGa wanda bai ba su abin sawa a bakaba.

6. Saboda haka kome zai zama dareda duhu, ba wahayi ko duba.Rana za ta fāɗi a kan annabawa,Yini zai zama musu duhu baƙiƙirin.

7. Masu gani za su sha kunya,Masu duba kuwa za su ruɗe,Dukansu za su rufe bakinsu,Gama ba amsa daga wurin Allah.

8. Amma ni ina cike da iko,Da Ruhun Ubangiji,Da shari'a da ƙarfin hali,Don in sanar wa Yakubu da laifinsa,Isra'ila kuma da zunubinsa.

9. Ku ji wannan, ya ku shugabanninjama'ar Yakubu,Da ku sarakunan mutanen Isra'ila,Ku da kuke ƙyamar shari'ar gaskiya,Kuna karkatar da dukan gaskiya.

10. Kuna gina Sihiyona da jini,Kuna kuwa gina Urushalima dazalunci.

11. Shari'ar shugabannin ƙasar ta cinhanci ce.Firistocinta suna koyarwa donneman riba,Haka kuma annabawa suna annabcidon neman kuɗi.Duk da haka suna dogara gaUbangiji, suna cewa,“Ai, Ubangiji yana tsakiyarmu,Ba masifar da za ta same mu.”

12. Saboda ku kuwa za a nome Sihiyonakamar gona,Urushalima kuwa za ta zama tsibinkufai,Dutse inda Haikali yake zai zamakurmi.

Karanta cikakken babi Mika 3