Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

M. Sh 33:2-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. Ya ce,“Ubangiji ya taho daga Sina'i,Daga Dutsen Faran kuma ya haskaka,Ya taho tare da dubban tsarkakansa,Da harshen wuta a damansa.

3. Hakika, yana ƙaunar jama'arsa,Dukan tsarkaka suna a ikonka,Suna biye da kai,Suna karɓar umarninka.

4. Musa ya ba mu dokoki,Abin gādo ga taron jama'ar Yakubu.

5. Ubangiji shi ne sarki a Yeshurun,Sa'ad da shugabanni suka taru,Dukan kabilan Isra'ila suka taru.

6. “Allah ya sa Ra'ubainu ya rayu, kada ya mutu,Kada mutanensa su zama kaɗan.”

Karanta cikakken babi M. Sh 33